Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Farfesa Umar Pate kan ranar yaki da gallazawa 'Yan Jaridu

Wallafawa ranar:

Yau ce Majalisar Dinkin Duniya ta ware a matsayin ranar yaki da gallazawa Yan Jaridu ta duniya, wanda ake amfani da ita wajen fadakar da jama’a kan muhimmancin aikin Jarida da kuma mutunta ma’aikatan.Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, a sakon da ya aike a wannan ranar, ya bayyana takaicin sa kan yadda ake kaiwa Yan Jaridu hari, inda yake cewa a cikin shekaru 10 da suka gabata, Yan Jaridu 1,010 aka kashe, kuma har ya zuwa yau ba’a hukunta kashi 90 na wadanda suka aikata kisan ba.Dangane da wannan rana, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Prof Umar Pate na Jami’ar Bayero, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.

Wasu 'yan jaridu a kasar India yayin zanga-zangar adawa da cin zarafinsu.
Wasu 'yan jaridu a kasar India yayin zanga-zangar adawa da cin zarafinsu. Indranil Mukherjee/AFP/Getty Images
Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.