Dr Sa’idu Ahmad Dukawa na Jami’ar Bayero kan takaddamar kisan Khashoggi a Istanbul
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:23
Shugaban Turkiya Recep Tayyib Erdogan ya bukaci hukumomin Saudiya su gaggauta bayyana wanda ya bada umarnin kisan gillar da aka yi wa dan jarida Jamal Kashoggi a ofishin jakadancin kasar da ke Istanbul, da kuma Karin bayani kan inda aka boye gawar dan jaridar.Jawabin na Erdogan ya zo ne a daidai lokacin da babban mai gabatar da kara na Saudiya ke shirin isa Istanbul dangane da batun gudanar da bincike kan kisan gillar da aka yi wa Kashoggi, dan jaridar da ya yi kaurin suna wajen sukar masarautar saudiyyar. Kan wannan batu da yaki ci yaki cinyewa muka tattauna da DR Sa’idu Ahmad Dukawa na Jami’ar bayero dake Kano a Najeriya.