Isa ga babban shafi
Saudiya-MDD

"A janye kariyar wadanda suka kashe Khashoggi"

Hukumar Kare Hakkin Bil’adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci janye rigar kariya ta hukumomin da ke da hannu a bacewar dan jaridan Saudiya, Jamal Khashoggi.

Jamal Khashoggi da ake zargin Saudiya da kashe shi
Jamal Khashoggi da ake zargin Saudiya da kashe shi MOHAMMED AL-SHAIKH / AFP
Talla

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, shugabar hukumar, Michelle Bachelet ta bayyana cewa, akwai bukakar janye rigar kariyar lura da girmar al’amarin da ke tattare da bacewar Khashoggi a ofishin jakadancin Saudiya a Turkiya.

Duk da cewa, akwai yarjejeniyar Vienna ta 1963 da ke kare hurumin ofisoshin jakadancin kasashen duniya, amma Hukumar Kare Hakkin Bil’adaman na bukatar daukan matakin janye kariyar wadanda ke da hannu a bacewar .

Tuni Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Mike Pompeo ya isa birnin Riyadh na Saudiya don tattaunawa da Sarki Salman kan bacewar dan jaridan.

Tun a ranar 2 ga watan Oktoba ne Khashoggi ya bacewa bayan tabbatar da shigarsa ofishin jakadancin Saudiya a birnin Santanbul na Turkiya, yayin da ake zargin hukumomin Saudiya da kitsa kashe shi saboda yadda yake sukar manufofin gwamnatin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.