Shugabannin duniya na halartar jana'izar Kofi Annan
Shugabannin kasashen duniya da sarakuna da dama na halartar jana’izar tsohon Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Kofi Annan a kasar Ghana.
Wallafawa ranar:
Ana bikin jana'izar ne bayan Ghana ta shafe kwanaki uku tana zaman makokin rashin tsohon jakadan na duniya da ya rasu yana da shekaru 81 bayan fama da gajeran rashin lafiya a gidansa na Switzerland.
Daga cikin masu halartar jana’izar sun hada da Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres da shugabannin kasashen Cote d’Ivoire da Liberia da Namibia da Habasha da Nijar da kuma Zimbabwe masu makwabtaka da Ghana.
Ana kuma saran tsoffin shugabannin kasahsen Jamus da Mauritius su halarci bikin jana’izar.
Tuni al’ummar Ghana ta yi bankwana cikin karrama da gawar marigayin.
Kofi Annan ya jagoranci Majalisar Dinkin Duniya tun daga shekarar 1997 zuwa 2006 kuma shi ne mutun na farko daga yankin Afrika da ke kudu da sahara da ya fara rike mukamin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu