Isa ga babban shafi
Iran

Iran zata gabatar da wani jirgin saman yaki da ta kera

Kasar Iran ta sanar da cewa cikin wannan mako da za ta kaddamar da wani jirgin sama na yaki mai muhimmanci, sannan kuma zata bada karfi wajen kera makamanta masu linzami.

ministan tsaron Iran, Janar Amir Hatami, na gabatar da wani makami mai cin matsaikacin zango da kasar ta kera  à Téhéran,  13 ogusta  2018.
ministan tsaron Iran, Janar Amir Hatami, na gabatar da wani makami mai cin matsaikacin zango da kasar ta kera à Téhéran, 13 ogusta 2018. AFP PHOTO / HO /IRANIAN DEFENCE MINISTRY WEBSITE
Talla

Ministan tsaro na kasar Brig. Janar Amir Hatami ne ya sanar da haka inda yake cewa, a ranar Laraba 21 ga watan ogusta ne da kasar za ta yi bukin ranar masanaantun da zaayi ne za’a gabatar da jirgin yakin.

Shugaba Donald Trump na Amurka dake adawa da dukkan matakan kara karfin da Iran ke yi , a watan 5 daya gabata ya janye Amurka daga cikin yarjejeniyar Nukliyar da manyan kasashen duniya suka kuklla da Iran a shekara ta 2015 don sassauta mata takunkumi .

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.