Isa ga babban shafi
Isra'ila-Falesdinawa

Majalisar Dinkin Duniya ta nemi tsagaita rikicin Hamas da Isra'ila

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci Israila da Kungiyar Hamas su dakatar da musayar wuta da suke yi a tsakaninsu wadda ke ci gaba da haddasa asarar rayukan Falasdinawa. Kiran wanda ke fitowa daga bakin Jakadan Majalisar na musamman a yankin Gaza, Nickolay Mladenov na zuwa ne sa'o'i kalilan bayan wasu hare-haren Isra'ila da suka hallaka Falasdinawa 4 a yau Juma'a.

Ka zalika Ma’aikatar lafiya a yankin na Gaza ta sanar da cewa Isra'ilan ta kuma hallaka Bafalasdine na hudu ne yayin zanga-zangar da ta gudane inda ta harbe matashin har lahira.
Ka zalika Ma’aikatar lafiya a yankin na Gaza ta sanar da cewa Isra'ilan ta kuma hallaka Bafalasdine na hudu ne yayin zanga-zangar da ta gudane inda ta harbe matashin har lahira. REUTERS/Suhaib Salem
Talla

Nickolay Mladenov ya bukaci sasantawa tsakanin bangarorin biyu da nufin kaucewar bunkasuwar rikicin da ka iya juyewa zuwa wani salo daban.

Hamas ta sanar da cewa Israila ta yi amfani da jiragen sama da kuma tankunan yaki  wajen kai farmaki yankin na Gaza, wanda nan ta ke ta hallaka Falasdinawa 4 bayan da ta yi luguden wuta kan jami'an da ke tsaron iyaka.

Ka zalika Ma’aikatar lafiya a yankin na Gaza ta sanar da cewa Isra'ilan ta kuma hallaka Bafalasdine na hudu ne yayin zanga-zangar da ta gudane inda ta harbe matashin har lahira.

Zanga-Zangar ta yau ita ce ta baya-bayan da Falasdinawan suka shafe watanni suna yi tun bayan ayyana kudus a matsayin babban birnin Israila, wanda ke barazana ga yiwuwar barkewar sabon yaki tsakanin Israilan da Hamas, Wadanda sukayi yaki har so uku cikin shekaru 10.

Sai dai a wata sanarwa da wani sojin Israila ya fitar, ta ce tun farko Falasdinawan ne suka fara harbe jami'ansu da ke tsaron kan Iyaka dalili kenan da ya tilasta musu daukar matakin ramuwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.