Mutane 100 sun mutu a ambaliyar ruwa a Japan
Firaministan Japan, Shinzo Abe ya soke ziyarar da ya shirya kaiwa kasashen ketare hudu bayan ambaliyar ruwa ta yi sanadiyar mutuwar mutane kimanin 100 a kasar.
Wallafawa ranar:
Mr. Abe ya shirya kai ziyarar aiki a kasashen Faransa da Belgium da Saudiya da kuma Masar daga ranar Laraba, amma ya soke saboda wannan ibtila’in da ya afka wa kasarsa kamar yadda ofishinsa ya sanar.
Jami’an agaji sun bayyana fargabar karuwar asarar rayuka, duba da yadda wasu kafofin yada labaran kasar suka rawaio cewa, har yanzu akwai tarin mutanen da suka bace.
Firaminista Abe, ya nuna damuwa kan jinkirin da ake samu wajen aikin ceto wadanda ibtila’in ya ritsa da su.
Sama da mutane miliyan biyu ne ambaliyar ruwan ta tilasta wa tserewa daga muhallansu, bayan manyan kogunan da suka tumbatsa suka shafi yankunan yammaci da tsakiyar kasar.
Hukumar Lura da Yanayi ta Japan ta yi gargadin cewa, akwai sauran hadari a gaba, ko da kuwa an samu sassaucin ruwan sama, domin kuwa yankunan da ambaliyar ta shafa na fuskantar barazanar zabtarewar kasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu