Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi alkawarin bayar da tallafin Dalar Amurka miliyan 75 don ci gaba da yaki da kungiyar Boko Haram a Najeriya da sauran kasashen da ke makwabtaka da ita. Macron wanda a karon farko kenan da yake ziyartar Najeriya a matsayin shugaban kasa, ya ce, gwamnatinsa za ta kuma bai wa Najeriyan bashin kudaden da yawansu ya kai Dala miliyan 475 don inganta harkokin sufuri a jihar Legas da samar da ruwan sha mai tsafta a jihar Kano, yayin da kuma za a bunkasa gandun dajin da ke jihar Ogun. Kabir Yusuf ya tattauna da mai magana da yawun shugaba Buhari, Garba Shehu wanda ya yi fashin baki kan ziyarar.
Sauran kashi-kashi
-
Mukhtar Bello kan rikicin siyasar Senegal
A wannan Juma’a ake kammala yakin neman zaben shugaban Senegal, kasar da rikicin siyasa da ya auku a cikinta a baya-bayan nan ya gaza yin mummunan tasiri a kanta duk kuwa da jan hankalin duniya da lamarin ya yi.22/03/202403:40 -
Yahuza Getso kan fargabar gwamnatin Najeriya na kai hari karin wasu makarantu
Yayin da ake ciki gaba da samun karuwar satar dalibai a Najeriya, Gwamnatin kasar ta bayyana fargabarta tare da yin gargadin cewa za’a iya kaiwa wasu makarantu a jihohin kasar 14 har da babban birnin tarayya Abuja.Shin hakan ya nuna gazawar gwamnatin kasa ta fannin tsaro kenan? Abdulkadir Haladu Kiyawa, ya tattauna da Dakta Yahuza Ahmad Getso masanin tsaro a Najeriyar.12/03/202403:25 -
Sheikh Sani Yahaya Jingir kan fa'idar azumin watan Ramadan
A yayin da alummar musulmi daga kasashe da dama na duniya suka fara Azumin watan Ramadan, daya daga cikin manyan malaman addninin musulunci a Nijeriya, Sheikh Muhamad Sani Yahaya Jingir, ya yi karin haske akan irin fa'idar dake tattare da Azumin watan Ramadan ga abun da yake cewa a zantawarsu da wakilinmu na Jos Tasiu zakari.11/03/202402:58 -
Saudatu Abubakar kan bikin ranar mata ta duniya
Ranar 8 ga watan Maris din kowacce shekara, rana ce da Majalisar Dinkin Duniya ta ware don bikin ranar mata da ke da aniyar lalubo matsalolin da mata ke fuskanta da kuma duba hanyoyin warware su.08/03/202403:31 -
Umar Alangawari kan kai wa motocin dakon kayan abinci da rumbuna hari
Batun kai hari tare da daka wawa kan rumbunan ajiyar kayayyakin abinci na hukumomi a wasu yankunan Najeriya na neman zama ruwan dare, la’akari da yadda a ‘yan kwanakin nan hakan ta rika faruwa, yayin da kuma a wasu lokutan aka rika tare motocin dakon abincin tare da afka musu, lamarin da ake alakantawa da tsananin tsadar rayuwa da yunwar da ke addabar dimbin mutane a Najeriya.05/03/202403:19