Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Garba Shehu kan ziyarar Macron a Najeriya

Wallafawa ranar:

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi alkawarin bayar da tallafin Dalar Amurka miliyan 75 don ci gaba da yaki da kungiyar Boko Haram a Najeriya da sauran kasashen da ke makwabtaka da ita. Macron wanda a karon farko kenan da yake ziyartar Najeriya a matsayin shugaban kasa, ya ce, gwamnatinsa za ta kuma bai wa Najeriyan bashin kudaden da yawansu ya kai Dala miliyan 475 don inganta harkokin sufuri a jihar Legas da samar da ruwan sha mai tsafta a jihar Kano, yayin da kuma za a bunkasa gandun dajin da ke jihar Ogun. Kabir Yusuf ya tattauna da mai magana da yawun shugaba Buhari, Garba Shehu wanda ya yi fashin baki kan ziyarar.

Shugaba Emmanuel Macron na Faransa da takwaransa na Najeriya Muhammadu Buhari
Shugaba Emmanuel Macron na Faransa da takwaransa na Najeriya Muhammadu Buhari Présidence du Nigéria /Reuters
Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.