Bakonmu a Yau
Dr Abdulkadir Suleiman Muhammad kan rikicin da ke tattare da mayar da Qudus babban birnin Isra'ila
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:16
Kasashen duniya na ci gaba da kiran ganin an kai zuciya nesa kan zanga zangar da Falasdinawa keyi yau kusa da iyakar Israila, wanda ya kaiga harbe 44 har lahira da kuma jikkata sama da 2,000. Kasashen Faransa da Birtaniya da kungiyar kasashen Turai duk sun bukaci taka tsan tsan.Bashir Ibrahim Idris ya zanta da Dr Abdulkadir Suleiman Muhammad kan arangamar da ta taso sakamakon bude ofishin Jakadancin Amurka a Birnin Kudus, kuma ga tsokacin da yayi akai.