Isa ga babban shafi
Isra'ila-Iran

Isra'ila ta kai wa dakarun Iran hari a Syria

Isra’ila ta kai hare-hare da makamai masu linzame a kan sansanonin sojin Iran da ke Syria, bayan da Isra’ilan ta yi zargin cewa wasu rokoki da aka kera a Iran sun fada a yankin tsaunukan Golan cikin daren jiya.

Isra'ila ta ce ta dauki matakin kai harin ne bayan ta zargi Iran da fara kai mata a hari a tsaunukan Golan
Isra'ila ta ce ta dauki matakin kai harin ne bayan ta zargi Iran da fara kai mata a hari a tsaunukan Golan AFP PHOTO/DAVID BUIMOVITCH
Talla

Rahotanni sun ce sojin Syria sun kakkabo wasu daga cikin makaman da Isra’ila ta cilla, yayin da wasu suka fada a kusa da birnin Damascus, to sai dai babu karin bayani a game da irin asarar da wadannan hare-hare suka haifar.

Isra’ilan ta ce, kimanin rokoki 20 dakarun juyin juya halin Iran suka cilla, abin da ta bayyana a matsayin daya daga cikin manyan hare-hare da aka kaddamar mata a cikin gomman shekaru da suka gabata.

Dama dai ana ganin Isra’ila na dakon harin ramako daga Iran tun bayan da dakarun Isra’ila suka hallaka dakarun Iran bakwai a wani hari a Syria a cikin watan Afrilu.

Harin makaman rokan na zuwa bayan shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da janyewar kasarsa daga yarjejeniyar nukiliyar Iran.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.