Birtaniya ta hallaka fararen hula a Syria
Birtaniya ta tabbatar da yadda wasu hare-harenta ta sama suka hallaka dimbin fararen hula a Syria. Sanarwar da ta fitar ta ce harin ya nufaci maboyar mayakan IS ne amma kuma aka kuskure tare da yin luguden wuta kan fararen hula.
Wallafawa ranar:
Wananna ne dai karon farko da Birtaniyar ta amsa laifinta na kai hari tare da hallaka fararen hular da basu ji ba basu gani ba, ko da ya ke dai a lokuta da dama tana dora laifin hakan kan gwamnatin Syria.
Sanarwar wadda Sakataren tsaron birtaniyar Gavin Williamson ya fitar, ta nuna cewa ko a ranar 26 ga watan Maris ma wasu jerin hare-haren birtaniyar a Maboyar mayakan IS 3 da ke yankin gabashin Ghouta sun hallaka wani mai babur da ya zo giftawa ta wajen.
Sanarwar Birtaniyar na zuwa ne bayan wata kafar yada labarai ta kwarmata yadda hare-haren na ta ke salwantar da rayukan fararen hula.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu