Isa ga babban shafi
Najeriya-Birtaniya

Muhammadu Buhari ya gana da Theresa May

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi wata ganawa ta musamman da Firaministar Birtaniya Theresa May yau Litinin. Ganawar na zuwa a dai dai lokacin da shugabannin kasashe renon Ingila ke wani taro a birnin na London.

Firaministar Birtaniya Theresa May tare da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a birnin Landan
Firaministar Birtaniya Theresa May tare da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a birnin Landan REUTERS
Talla

Tattaunawar dai tsakanin bangarorin biyu ta shafi alakar da ke tsakanin Birtaniyar da Najeriya kamar yadda mataimakin shugaban na musamman kan kafofin sada zumunta Bashir Ahmad ya wallafa a Shafinsa na Twitter.

Muhammadu Buhari yayin ganawar ya kuma yabawa Teresa May kan kokarin da Birtaniya ke yi na horar da jami'an soji don kammala fatattakar kungiyar ta'addanci ta Boko Haram.

Shugabannin biyu ana saran za kuma su kara yin wata kebantacciyar ganawa ta musamman a taron kasashe renon Ingila da zai gudana a birnin na London.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.