Muhammadu Buhari ya gana da Theresa May
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi wata ganawa ta musamman da Firaministar Birtaniya Theresa May yau Litinin. Ganawar na zuwa a dai dai lokacin da shugabannin kasashe renon Ingila ke wani taro a birnin na London.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Tattaunawar dai tsakanin bangarorin biyu ta shafi alakar da ke tsakanin Birtaniyar da Najeriya kamar yadda mataimakin shugaban na musamman kan kafofin sada zumunta Bashir Ahmad ya wallafa a Shafinsa na Twitter.
Muhammadu Buhari yayin ganawar ya kuma yabawa Teresa May kan kokarin da Birtaniya ke yi na horar da jami'an soji don kammala fatattakar kungiyar ta'addanci ta Boko Haram.
Shugabannin biyu ana saran za kuma su kara yin wata kebantacciyar ganawa ta musamman a taron kasashe renon Ingila da zai gudana a birnin na London.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu