Isa ga babban shafi
Saudiya

An gudanar da gasar tseren keke ta mata karon farko a Saudiya

A Karon farko kasar Saudi Arabia ta gudanar da gasar tseren keke na mata, a karkahsin sauye sauyen da Yariman kasar, Muhammad ibn Salman ke aiwatar wa.

Wannan ne karon farko da aka gudanar da gasar tseren keken na mata a Saudiyya.
Wannan ne karon farko da aka gudanar da gasar tseren keken na mata a Saudiyya. Fabien Jannic-Cherbonnel/RFI
Talla

Rahotanni sun ce an gudanar da tseren kekunan ne a birnin Jeddah da ke kasar ta Saudi Arabia, inda mata 47 suka shiga gasar ta kilomita 10.

Wadda ta shirya gasar Nadima Abu al-Enein ta ce ta yi mamakin ganin yawan matan da suka shiga gasar, wanda a shekarun baya abu ne mai wuya a fadin kasar.

Nadima ta ce da an shirya mata 30 za su shiga gasar, amma kuma ganin yawan matan da suka fito ya sa suka kara zuwa 47.

Kasar Saudi Arabia na ci gaba da ganin sauye sauye tun bayan kama mulkin Sarki Salman bin Abdulaziz, wanda ya nada dan sa Muhammad a matsayin Yarima mai jiran gado.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.