Rashawa na kai wa Facebook hari
Shugaban shafin Facebook, Mark Zuckerberg ya shaida wa mambobin Majalisar Dattawan Amurka cewa, kamfaninsa na fafatawa da wasu mutanen Rasha da ke kokarin amfani da dandalin na facebook don cimma muradinsu.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Zuckerberg ya ce,wannan yaki ne da makami, kuma Rashawan za su ci gaba da inganta ayyukansu.
Zuckerberg da ke shan tambayoyi kan kutsen bayanan sirrin mutane miliyan 50 a shafin facebook, ya kuma ce, Robert Mueller da ke binciken zargin kutsen Rasha a zaben Amurka, ya yi wa ma'aikatan kamfanin wasu tambayoyi.
Ko da yake shugaban na Fcebook ya ce, ba ya cikin wadanda aka yi wa tambayoyin.
A bangare guda, Zuckerberg ya nemi afuwa dangane da yadda aka saci bayyanan milyoyin mutanen da ke amfani da shafin ba tare da saninsu ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu