Isa ga babban shafi
Najeriya

Birtaniya, kasashen Turai ba sa adawa da takarar Buhari a 2019

Kasar Birtaniya ta ce, ba ta adawa da takarar shugaban Najeriya Muhammadu Buhari na neman wa’adi na biyu a zaben kasar na shekara mai zuwa.

Kasashen yammacin duniya sun ce ba sa adawa da takarar Buhari a zaben shugabancin kasar mai zuwa
Kasashen yammacin duniya sun ce ba sa adawa da takarar Buhari a zaben shugabancin kasar mai zuwa REUTERS/Vincent Kessler
Talla

Jakadan Birtaniya a Najeriya, Paul Arkwright ya shaida wa jaridar Premium Times cewa, Birtaniya da daukacin kasashen Yammacin duniya ba sa adawa da takarar shugaban na Najeriya.

Arkwright ya yi watsi da zargin cewa, kasashen Yammacin duniya ba sa tare da shugaban Najeriya kan shirin takarar neman wa’adi na biyu, in da yake cewa 'yan Najeriya ne ke da hurumin yanke hukunci kan takarar ta shi.

Ya zuwa yanzu shugaban Najeriya Muhammadu Buhari bai fito karara ya bayyana shirin yin takara a zaben shekara mai zuwa ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.