Isa ga babban shafi
Syria

Jamus da Faransa sun bukaci matsin lamba kan Syria

Shugabannin Jamus da Faransa sun bukaci Rasha da ta tsananta matsin lamba kan gwamnatin Syria don ganin ta aiwatar da yarjejeniyar tsagaita musayar wuta ta Majalisar Dinkin Duniya a kasar.Wannan na zuwa ne bayan dakarun kasar sun sake kaddamar da sabon farmaki kan fararen hula a yankin Ghouta.

Fararen hula 500 sun mutu a mako guda a yankin gabashin Ghouta
Fararen hula 500 sun mutu a mako guda a yankin gabashin Ghouta REUTERS/ Bassam Khabieh
Talla

Shugabar gwamnatin Jamus, Angela Merkel da takwaranta na Farasa, Emmanuel Macron sun tattauna da shugaba  Putin na Rasha ta wayar tarho, in da suka jaddama masa muhimmancin gaggauta aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Syria mai fama da rikici.

Wata sanarwa da ta fito daga ofishin gwamnatin Jamus ta ce, Uwargida Merkel da Macron da Putin duk sun yi madalla da yarjejeniyar tsagaita musayar wuta ta kwanaki 30, musamman don bada damar shigar da kayayyakin agaji tare da kwashe fararen hula daga yankin da yaki ya kazanta.

Shugabannin sun gana ne bayan Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya  ya bukaci cimma yarjejeniyar ta kwanaki 30 a Syria a ranar Asabar.

Sai dai bayan wannan zama, dakarun gwamnatin Syria sun sake kai farmaki a Ghouta tare da kashe fararen 41 kamar yadda kungiyar da ke sa ido a Syria mai cibiya a Birtaniya ta sanar.

Sama da fararen 500 ne ake zaton sun rasa rayukansu a cikin mako guda sakamakon barin wutar da dakarun gwamnatin Syria suka yi a yankin gabashin Ghouta da ke kusa da birin Damascus.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.