Mu Zagaya Duniya
Halin da ake ciki dangane da sace daliban makarantar mata da ke garin Dapchi
Wallafawa ranar:
Kunna - 20:08
Shirin Mu Zagaya Duniya na wannan makon, kamar yadda aka saba ya yi bitar wasu daga cikin manyan labarun da suka faru ne a duniya. Daga cikin manyan labaran da shirin ya yi bita akwai halin da ake ciki, a jihar Yobe da ke Najeriya, bayan sace daliban makarantar sakandaren 'yan mata ta Dapchi da ake zargin mayakan Boko Haram ne suka sace su.