Isa ga babban shafi

Amnesty ta fitar da rahoton shekara kan cin hanci a kasashen duniya

Kungiyar Transparency dake yaki da cin hanci da rashawa a duniya, ta fitar da rahotan ta na shekara shekara, wanda ke nuna kasashen da aka fi samun cin hanci a duniya.

Tutar Amnesty International.
Tutar Amnesty International. Reuters
Talla

Shugaban kungiyar, Delia Ferreira Rubio tace ba’a samu ci gaba a kasashe da dama ba, kan matakan da suke dauka na dakile matsalar cin hanci a cikin shekaru 6 da suka gabata.

Kungiyar tace cin hancin na take hakkokin jama’a da kuma bin doka da oda, wanda ke nuni da dangantaka tsakanin gaskiya da dimokiradiya.

Kungiyar ta bayyana kasashen Senegal, Cote d’Ivoire da kuma Birtaniya a matsayin wadanda suka samu ci gaba, yayin da kasashe irin su Syria da Yemen da ake fama da tashin hankali suka kara samun koma baya.

Kasashen da cin hancin yayi kamari sun hada da Somalia, Sudan ta Kudu, Syria, Afgahnistan, Yemen, Sudan, Libya, Koriya ta Arewa, Venezuela da kuma Iraqi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.