Isa ga babban shafi
NATO

Stoltenberg ya gargadi kasashen EU kan NATO

Sakataren kungiyar tsaro ta NATO Jens Stoltenberg, ya gargadi kasashen Turai da su yi hattara, ka da sabon kawancen tsaron da suka kulla a tsakaninsu ya gurgunta ayyukan kungiyar ta NATO.

Sakataren kungiyar tsaro ta Jens Stoltenberg
Sakataren kungiyar tsaro ta Jens Stoltenberg REUTERS/Eric Vidal
Talla

Jens Stoltenberg, ya bayyana wannan shakku ne a dai dai lokacin da ministocin tsaron kasashe mambobi a kungiyar ta NATO ke shirin gudanar da taro a birnin Brussels a wannan Laraba.

A cikin watan Disamban da ya gabatar ne kasashen na Turai suka sanar da kulla kawance domin karfafa tsaro a tsakaninsu, duk da cewa dukkaninsu mambobi ne a kungiyar ta NATO, lamarin da wasu ke ganin cewa zai iya haddasa matsala ga manyan manufofin kungiyar.

Amurka dai na daya daga cikin kasashen da ke sukar sabon kawacen tsaron na kasashen Turai, tare da kafa hujjar cewa hakan zai iya rage adadin kudaden da suke bai wa kungiyar NATO domin daukar dawainiyar NATO.

Duk da kokarin da kasashen na Turai ke yi domin jaddada NATO a matsayin wadda za ta ci gaba da tabbatar da tsaronsu, manazarta na ganin abin da kamar wuya tauna taura biyu a baki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.