Birtaniya ta bukaci gudanar da bincike a kisan Rohingya
Sakataren Harkokin Wajen Birtaniya Boris Johnson ya bukaci gudanar da bincike mai zaman kansa domin gano wadanda suka aikata aika-aika kan Musulmai ‘yan Kabilar Rohingya a kasar Myanmar.
Wallafawa ranar:
Johnson wanda ya ziyarci kasar, ya gana da jagorar gwamnatin kasar Aung San Suu Kyi wadda kimarta ta zube a idon duniya saboda yadda ta kawar da kai lokacin da ake cin zarafin dubban ‘yan Rohingya.
Sakataren ya bayyana cewar, ya bukaci hukumomin kasar da su gudanar da bincike domin hukunta duk wanda yake da hannu a cin zarafin.
Kungiyar agaji ta Reporters Without Borders ta ce, akalla ‘yan kabilar Rohingya dubu 6 da 700 aka kashe lokacin da rikicin ya barke, yayin da sama da dubu 750 suka nemi mafaka a Bangladesh.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu