Isa ga babban shafi
Myanmar

Birtaniya ta bukaci gudanar da bincike a kisan Rohingya

Sakataren Harkokin Wajen Birtaniya Boris Johnson ya bukaci gudanar da bincike mai zaman kansa domin gano wadanda suka aikata aika-aika kan Musulmai ‘yan Kabilar Rohingya a kasar Myanmar.

Sakataren Harkokin Wajen Birtaniya Boris Johnson tare da Musulaman Rohingya a Myanmar
Sakataren Harkokin Wajen Birtaniya Boris Johnson tare da Musulaman Rohingya a Myanmar © Reuters
Talla

Johnson wanda ya ziyarci kasar, ya gana da jagorar gwamnatin kasar Aung San Suu Kyi wadda kimarta ta zube a idon duniya saboda yadda ta kawar da kai lokacin da ake cin zarafin dubban ‘yan Rohingya.

Sakataren ya bayyana cewar, ya bukaci hukumomin kasar da su gudanar da bincike domin hukunta duk wanda yake da hannu a cin zarafin.

Kungiyar agaji ta Reporters Without Borders ta ce, akalla ‘yan kabilar Rohingya dubu 6 da 700 aka kashe lokacin da rikicin ya barke, yayin da sama da dubu 750 suka nemi mafaka a Bangladesh.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.