Isa ga babban shafi
Falasdinu

Mahmud Abbas na ganawa da EU kan Falasdinu

Shugaban Falasdinu Mahmud Abbas na shirin gabatar da bukatarsu ga Kungiyar Tarayar Turai ta neman su amince da kasar Falasdinu a matsayin mai cin gashin kanta.

Shugaban Falasdinawa Mahmoud Abbas
Shugaban Falasdinawa Mahmoud Abbas AFP/Abbas Momani
Talla

Bayanai na cewa Mahmud Abbas zai gabatar da wannan bukata ce a yau Litinin a birnin Brussels a yayin ganawarsa da ministocin kasashen waje na Kungiyar Tarayyar Turai.

Ministan wajen Falastdinu, Riad al-Malki ya ce, Abbas zai nemi kasashen Turai su dauki matakin ne a matsayin mayar da martini ga shugaban Amurka Donald Trump da ke sanar da amincewarsa da birnin Kudus a matsayin babban birnin kasar Isra'ila.

Kazalika Abbas zai bukaci shugabar diflomasiyar Kungiyar Tarayyar Turai, Federica Mogherini da sauran ministocin nahiyar 28 don ganin cewa sun kara kaimi a rawar da suke takawa wajen samar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.