Mahmud Abbas na ganawa da EU kan Falasdinu
Shugaban Falasdinu Mahmud Abbas na shirin gabatar da bukatarsu ga Kungiyar Tarayar Turai ta neman su amince da kasar Falasdinu a matsayin mai cin gashin kanta.
Wallafawa ranar:
Bayanai na cewa Mahmud Abbas zai gabatar da wannan bukata ce a yau Litinin a birnin Brussels a yayin ganawarsa da ministocin kasashen waje na Kungiyar Tarayyar Turai.
Ministan wajen Falastdinu, Riad al-Malki ya ce, Abbas zai nemi kasashen Turai su dauki matakin ne a matsayin mayar da martini ga shugaban Amurka Donald Trump da ke sanar da amincewarsa da birnin Kudus a matsayin babban birnin kasar Isra'ila.
Kazalika Abbas zai bukaci shugabar diflomasiyar Kungiyar Tarayyar Turai, Federica Mogherini da sauran ministocin nahiyar 28 don ganin cewa sun kara kaimi a rawar da suke takawa wajen samar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu