Isa ga babban shafi
Iraqi

Harin kunar bakin wake ya kashe mutane 35 a Bagadaza

Akalla mutane 35 sun rasa rayukansu a wasu tagwayen hare-haren kunar bakin wake a birnin Bagadaza na Iraqi kamar yadda majiyar likitoci ta sanar.

A karo na biyu kenan da ake kai farmaki cikin kwanaki uku a birnin Bagadaza na Iraqi
A karo na biyu kenan da ake kai farmaki cikin kwanaki uku a birnin Bagadaza na Iraqi 路透社
Talla

Ma’aikatar cikin gidan kasar ta ce, wasu mutane biyu ne sanye da jigidar bama-bamai suka kai harin na yau a dandalin Tayaran.

Harin shi ne na biyu a cikin kwanaki uku, yayin da sama da mutane 90 suka samu rauni.

Tun lokacin da mayakan ISIS suka mamaye wasu yankuna a shekarar 2014 a Iraqi, birnin Bagadaza ke fama da hare-haren bama-bamai.

Sai dai an samu sassaucin farmakin bayan sanarwar da gwamnatin kasar ta bayar da ke cewa, ta karbe dukkanin wuraren da ke karkashin ikon ISIS a watan jiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.