Isa ga babban shafi
Isra'ila

Isra'ila ta kaddamar da sabon shirin korar bakin-haure

Gwamnatin Isra’ila ta ce zata biya kudade ga dubban bakin-haure ‘yan nahiyar Afrika da ke kasar ba bisa ka’ida ba, domin komawa zuwa kasashensu. Isra’ila ta yi tayin hade da barazanar daure dukkanin bakin-hauren da ta kama a kasar a karshen watan Maris.

Firminstan Isra’ila Benjamin Netanyahu Ya ce kafin wannan lokacin sun kori bakin-haure 20000.
Firminstan Isra’ila Benjamin Netanyahu Ya ce kafin wannan lokacin sun kori bakin-haure 20000. REUTERS/Tsafrir Abayov/Pool
Talla

A farkon wannan mako ne aka kaddamar da sabon tsarin biyan dala dubu 3,500 ga kowane daga cikin bakin Hauren, sai kuma sama musu tikitin jirgi kyauta zuwa kasashensu na ainahi ko kuma wasu kasashen, wadanda kungiyoyin masu fafutukar kare hakkin dan adam suka ce ba za su wuce kasashen Rwanda da Uganda ba.

Mafi akasarin bakin-hauren da ke zaune a Isra’ila sun fito ne daga kasashen Eritrea da kuma Sudan, wadanda suka tsere daga azabtarwa da kuma rikicin da ake gwabzawa a yankunan da suka fito, sai kuma matsalar tattalin arziki.

Wani jami’in hukumar shige da fice na Israi’la da ya nemi a sakaya sunansa ya ce a halin da ake ciki, bakin-haure dubu 38,000 ne suka zaune a kasar ba bisa ka’ida ba, yayinda ake tsare da wasu dubu 1,420 a wasu manyan sansanoni biyu da aka tanada domin hakan.

Kafin wannan lokacin dai Firminstan Isra’ila Benjamin Netanyahu Ya ce kafin wannan lokacin sun kori bakin-haure 20000.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.