Isa ga babban shafi
Amurka-Duniya

Majalisar Dinkin Duniya ta yi watsi da matsayin Amurka

Majalisar Dinkin Duniya da gagarumar rinjaye ta yi watsi da matsayin Amurka na bayyana Birnin Kudus a matsayin babban birnin Israila.Duk da barazanar janye tallafi da Amurka ta yiwa kasashen duniya, kasashe 128 suka kada kuri’ar watsi da matsayin na Amurka.

Zauren majalisar Dinkin Duniya a birnin New york
Zauren majalisar Dinkin Duniya a birnin New york 路透社。
Talla

Kasashe 128 suka kada kuri’ar kin amincewa da matsayin na Amurka daga cikin kasashen duniya 193 dake Majalisar,yayin da kasashe 9 suka ki,kana kasashe 35 suka kauracewa kada kuri’a.

Cikin kasashen da suka goyi bayan Amurka, sun hada da Guatamala da Honduras da Togo, yayin da kasashe irin su Argentina da Canada da Mexico da Philipines da Romania da Rwanda suka kauracewa kada kuri’a.

Jakadiyar Amurka Nikki Haley ta bayyana cewa babu abinda zai canja dangane da matsayin Amurka.

Amurka za ta sanya ofishin jakadanci ta a Birnin Kudus, shine abinda Amurkawa suke so, kuma shine matakin da ya dace a cewar Halley.

Wakilin Falesdinu a Zauren ya bayyana vewa

sun hadu ne ba da manufar kiyaya ba ga Amurka, sai dai don tabbatar da gaskiya da kuma abinda ya dace wanda kasashen duniya suka amince da shi

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.