Isa ga babban shafi
cpj

Adadin ƴan Jaridun da ake ɗaurewa a shekara ya tashi-CPJ

Ƙungiyar da ke kare haƙƙoƙin ƴan Jaridu ta duniya, CPJ ta ce, adadin ƴan Jaridun da aka ɗaure a shekarar 2017 ya sake tashi, in da sama da rabin su suka fito daga ƙasashen Turkiya da China da kuma Masar.

Ƙungiyar CPJ na taka muhimmiyar rawa wajen kare haƙƙoƙ in yan jaridu a duniya
Ƙungiyar CPJ na taka muhimmiyar rawa wajen kare haƙƙoƙ in yan jaridu a duniya Reuters
Talla

Rahotan ƙungiyar na shekara da ta fitar a yau, ya nuna cewar ƴan Jaridu 262 aka tsare a cikin wannan shekara, wanda ya zarce na bara 259.

Rahotan ya ce, Turkiya da China da Masar kawai sun ɗaure 134 wanda ya zarce kashi 51 cikin 100 na bana.

Alkaluman sun nuna cewar Turkiya ta ɗaure ƴan Jaridu 73,in da China ta daure 41 a bana, yayin da  Masar da ta daure 20.

Ana yawan cin zarafin ƴan Jaridu a yayin gudanar da ayyukansu na sanar da al’umma kan halin da duniya ke ciki, in da wani lokacin su ke rasa rayukansu, yayin da wasu ke samun rauni baya ga lalata kayayyakin aikinsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.