Isa ga babban shafi
Lebanon

Hariri zai koma Lebanon a makon gobe

Firaministan Lebanon mai murabus Sa’ad Hariri ya bayyana cewa, zai koma birnin Beirut nan da kankanin lokaci don halartar bikin ranar samun ‘yancin kasar a ranar Laraba mai zuwa.

Firaministan Lebanon mai murabus Saad Hariri tare da shugaban Faransa Emmanuel Macron a fadar gwamnatin Faransa ta Elysée
Firaministan Lebanon mai murabus Saad Hariri tare da shugaban Faransa Emmanuel Macron a fadar gwamnatin Faransa ta Elysée REUTERS/Gonzalo Fuentes
Talla

Wannan na zuwa a yayin da kasar ta  fada  cikin rikicin siyasa tun bayan da ya sanar da matakinsa na yin murabus a Saudiya.

Hariri ya sanar da shirinsa na komawa Lebanon ne bayan ganawarsa da shugaban Faransa Emmanuel Macron a birnin Paris a yau Asabar.

Mr. Hariri ya kara da cewa, zai taka rawa a bikin samun ‘yancin kan kasarsa, sannan kuma zai sanar da matsayarsa akan lamurran siyasar kasar bayan ganawar da zai yi da shugaba Michel Aoun.

Shugaban Faransa Emmanuel Macrona na kokarin samar da matsalaha ce game da rikicin siyasar Lebanon.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.