Isa ga babban shafi
Libya-EU

"Yarjejeniyar EU da Libya kan bakin-haure abin takaici ce"

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana yarjejeniyar da kungiyar kasashen Turai EU ta kulla da Libya, domin hana baki kwarara nahiyar Turai ta tekun Meditareniya a matsatyin abin takaici, saboda yadda ake cin zarafin bakin.

Wasu daga cikin bakin-haure da ke tsare a daya daga cikin cibiyoyin hukumar a Tripoli, wadda ke kokarin dakile kwarararsu zuwa turai, ta kasar Libya. 10 ga Satumba Septemba, 2017.
Wasu daga cikin bakin-haure da ke tsare a daya daga cikin cibiyoyin hukumar a Tripoli, wadda ke kokarin dakile kwarararsu zuwa turai, ta kasar Libya. 10 ga Satumba Septemba, 2017. REUTERS/Hani Amara/File Photo
Talla

Shugaban hukumar kare hakkin Dan Adam ta majalisar Zeid Ra’ad Al Hussein, ya bayyana damuwa kan azabar da bakin-hauren ke fuskanta, a wuraren da ake tsare da su a Libya.

Jami’in yace babu yadda za’a yi kasashen duniya su zuba ido suna kallon irin cin zarafin da bakin ke fuskanta a Libya.

Hukumar dake yaki da bakin a kasar ta Libya, tace yanzu haka tana tsare da baki 19,900 daga kari kan 7,000 na watan jiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.