Rikicin Rohingya a Myanmar
Kusan 'yan kabilar Rohingya miliyan daya ne suka tsere zuwa Bangladesh sakamakon tashin hankalin da ya cika da su a jihar Rakhine da ke Myanmar. Majalisar Dinkin Duniya ta zargi sojojin Myanmar da kokarin share wata al'umma dag doran kasa ganin irin mummunar kisan da suka yi a Rakhine. Rikicin na baya-bayan nan ya samo asali ne bayan 'yan tawayen Rohingya sun kai hari kan wani ofishin jami'an 'yan sandan kasar a cikin wata Agustan da ya gabata.