Azoulay ta lashe kujerar hukumar UNESCO
An zabi tsohuwar Ministar al’adu ta Faransa, Audrey Azoulay a matsayin sabuwar Darekta Janar ta hukumar bunkasa ilimi, kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya bayan ta doke abokin takararta a zagaye na biyar , wato Hamad Abdul-Aziz al-Kawari na Qatar.
Wallafawa ranar:
Azoulay mai shekaru 45 za ta kasance mace ta biyu a tarihi da ta jagoranci hukumar UNESCO, yayin da ta samu kuri’u 30 akan al-Kawari da ya samu 28.
Nasarar Azoulay na zuwa ne bayan Amurka da Isra’ila sun sanar da shirinsu na janyewa daga hukumar ta UNESCO saboda tarin matsalolin siyasa da suka addadi hukumar.
Sai dai ana saran sabuwar shugabar za ta yi kokarin shawo kan Amurka da Isra’ila don ganin cewa sun ci gaba da zama mamba.
Al-Kawari ya gaza kai wa ga gaci ne a zaben wanda aka gudanar a birnin Paris na Faransa a jiya jumma’a bayan kasashen yankin Gulf da ke kawance da Saudiya sun ki jefa ma sa kuri’u.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu