Isa ga babban shafi
Faransa-Afrika

'Yan Afrika na shirin gurfanar da Sarkozy na Faransa

Kungiyoyin fara hula da dama ne daga kasashen Afrika suka yanke shawarar gurfanar da tsohon shugaban Faransa Nicolas Sarkozy a gaban kotun Duniya da ke Hauge, bisa zargin cewa shi ne ya jagoranci aikin kashe tsohon shugaban Libya Mu’ammar Gaddafi, lamarin da kuma ya yi sanadiyyar bazuwar makamai zuwa kasashe da dama na Afirka.

Tsohon shugaban Faransa Nicolas Sarkozy
Tsohon shugaban Faransa Nicolas Sarkozy GEORGES GOBET / AFP
Talla

Shahararren mawakin Afrika Tiken Jah Fakoli, shi ne ya jagoranci taron da kungiyoyin suka gudanar a birnin Bamako na kasar Mali.

A zantawarsa da RFI, Fakoli ya ce, lalle ya kamata a hukunta Nicolas Sarkozy saboda da dama daga cikin tsoffin jami’an gwamnatin Gaddafi sun fara magana.

A cewarsa, kisan da aka yi wa Kanar Gaddafi, ba wani abu ba ne face daukar fansa domin huce fushi.

"A sassa da dama na Afrika za ka tarar da makamai da aka wawashe daga Libya bayan kashe Gaddafi, hatta kungiyoyin ‘yan ta’adda sun amfana da wannan kisa domin sun samu dimbin makamai da suka yi amfani da su don wargaza zaman lafiya a Mali da sauran kasashe" in ji Fakoli.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.