Amurka ta janye wa Sudan takunkuman shekaru 20
Gwamnatin Sudan ta yi madalla da matakin da Amurka ta dauka na kawo karshen takunkuman karayar tattalin arziki da ta kakaba ma ta har tsawon shekaru 20.
Wallafawa ranar:
Sudan ta kuma bukaci Amurka da ta janye kasar daga jerin sunayen kasashen da ta ce, suna tallafa wa ayyukan ta’addanci.
A cewar, Amurka ta dauki matakin janye takunkuman ne saboda ci gaban da Sudan ta samu wajen mutunta hakkin dan Adam.
Daukan matakin na zuwa ne bayan kasashen biyu sun shafe tsawon watanni suna ganawar diflomasiya wadda aka fara ta tun lokacin shugabancin Barack Obama da ya mika wa Donald Trump mulki.
Ana ganin janye takunkuman zai taimaka wajen farfado da tattalin arzikin Sudan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu