Isa ga babban shafi
Sudan

Amurka ta janye wa Sudan takunkuman shekaru 20

Gwamnatin Sudan ta yi madalla da matakin da Amurka ta dauka na kawo karshen takunkuman karayar tattalin arziki da ta kakaba ma ta har tsawon shekaru 20.

Shugaban Sudan Omar al-Bashir
Shugaban Sudan Omar al-Bashir REUTERS/Mohamed Nureldin Abdallah
Talla

Sudan ta kuma bukaci Amurka da ta janye kasar daga jerin sunayen kasashen da ta ce, suna tallafa wa ayyukan ta’addanci.

A cewar, Amurka ta dauki matakin janye takunkuman ne saboda ci gaban da Sudan ta samu wajen mutunta hakkin dan Adam.

Daukan matakin na zuwa ne bayan kasashen biyu sun shafe tsawon watanni suna ganawar diflomasiya wadda aka fara ta tun lokacin shugabancin Barack Obama da ya mika wa Donald Trump mulki.

Ana ganin janye takunkuman zai taimaka wajen farfado da tattalin arzikin Sudan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.