Isa ga babban shafi
Syria

Za a kara samar da tudun muntsira a Syria karo na 4

Kasashen Rasha da Iran da Turkiya sun amince su sake samar da tudun muntsira a Yankin Idlib wanda shine na 4 a Syria, a kokarin da Moscow wacce ke jagorancin zaman ke yi wajen ganin ta kawo karshan yakin basasan kasar.

Wannan dai shi ne zai kasance tudun muntsira karo na hudu da ake kafawa a kasar ta Syria da yaki ya tagayyara, duk dai don samawa fararen hula mafaka..
Wannan dai shi ne zai kasance tudun muntsira karo na hudu da ake kafawa a kasar ta Syria da yaki ya tagayyara, duk dai don samawa fararen hula mafaka.. Reuters
Talla

A wata sanarwar hadin-gwiwa da suka fitar bayan taron kwananki 2 a Kazakhstan, kasashen 3 sun cim-ma matsayar tura dakarunsu yankin Idlib da ‘yan tawaye ke rike da shi domin bada kariya da wasu yankunan makwabta da suka hada da Latakia da Hama da Aleppo.

Tattaunawar da akayi a birnin Astana na Kazakhstan shine na 6 da Rasha ke jagoranta a cikin wannan shekarar a kokarin da ta ke wajen kawo karshan zub da jinni a kasar da yakin shekaru 6 ya tagayara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.