Mutane sun jikkata a wata fashewa a London
Jami’an ‘yan sandan birnin London na gudanar da bincike kan wata fashewa da aka samu a layin dogo na karkashin kasa da ke dandalin Parsons, in da mutane da dama suka samu rauni.
Wallafawa ranar:
‘Yan sandan na kallon lamarin da ta’addaci, yayin da mutane da dama suka samu raunin na kunar wuta a fuskokinsu, in da wasu kuma suka jikkata saboda tirmitsitsi.
Jami’an tsaron da ke yaki da ta’addanci ne ke jagorantar gudanar da bincike kan lamarin.
Kamfanin Dillancin Labrai na Reuters ya rawaito cewa, motocin daukan marasa lafiya da injinan kashe wuta da jirage masu saukar ungulu sun isa tashar layin dogon.
Firaministar Birtaniya Theresa May ta ce, tana tare da wadanda suka jikkata da kuma jamian agajin gaggawa da suka kai dauki.
Magajin garin birnin London, Sadiq Khan ya bukaci jama’a da su kwantar da hankukansu, in da ya ce, babu wata barazanar ta’addanci da za ta tsorata su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu