Trump ya gana da 'yan Democrat kan shirin DACA
Manyan ‘yan Majalisun Jam’iyyar Democrat a Amurka sun ce sun samu fahimtar juna a tattaunawar da suka yi da shugaba Donald Trump kan dokar da ya soke wadda ke kare bakin da suka shiga Amurka suna kananan yara.
Wallafawa ranar:
Shugaban marasa rinjaye a Majalisar Dattawar, Chuck Schumer da takwararsa a Majalisar Wakilai Nancy Pelosi sun ce, za su samar da dokar da za ta kare irin wadannan baki da kuma dokar kare iyakokin Amurka.
Sai dai bangarorin biyu ba su cimma matsaya ba kan shirin Trump na gina katanga tsakanin Amurka da Mexico.
Fadar shugaba Trump ta ce, shugaban zai ci gaba da janyo hankalin Majalisar domin samun goyan bayanta kan shirin gina katangar.
A farkon wannan watan ne, shugaba Trump ya sanar da matakin soke shirin da aka fi sani da DACA wanda gwamnatin Barack Obama ta samar don bai wa dubban kananan yara 'yan gudun hijira damar zama a Amuka duk da cewa ba su da takardun izinin zama.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu