Kotun Amurka ta amince da dokar hana shigar baki
Kotun kolin Amurka ta bai wa shugaba Donald Trump damar aiwatar da dokarsa ta hana baki shiga cikin kasar daga kasashen duniya.
Wallafawa ranar:
Alkalan kotun sun amince da bukatar gwamnatin Trump ta soke hukuncin da wata kotun daukaka kara ta yanke a can baya, in da ta yi watsi da matakin shugaban na hana shiga baki shiga cikin Amurka.
Gwamnatin Trump ta nuna fargabar cewa, hukuncin kotun daukaka karar zai bai wa wasu bakin haure kimanin dubu 24 damar shiga kasar.
Sai dai sabon hukuncin da kotun kolin ta yanke na a matsayin kwarya-kwaryar nasara ga shugaba Trump kafin nan da watan Oktoba mai zuwa, lokacin da babbar kotu za ta kammala zaman sauraren wata kara ta daban kan ingancin takardar umarni da Trump ya sanya wa hannu don haramta kasashen Musulmi 6 shiga cikin Amurka.
Kasashen sun hada da Iran da Libya da Somalia da Sudan da Syria da kuma Yemen.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu