Isa ga babban shafi
Amurka-Rasha-China

Kim Jong Un ya jikirta kai hari tsibirin Guam

Kasashen China da Rasha sun bukaci gudanar da tattaunawa domin rage tankiyar da ake samu tsakanin Amurka da Koriya ta Arewa bayan da shugaba Kim Jong-Un ya jinkirta kai harin tsibirin Guam.

Kim Jong Un Shugaban kasar Koriya ta Arewa
Kim Jong Un Shugaban kasar Koriya ta Arewa KCNA/via REUTERS
Talla

 China  kasar da tafi kusanta da Koriya ta Arewa tace rikicin Amurka da Koriya ya kai wani matakin dake bada tsoro, saboda haka lokaci yayi da ya kamata a je teburin tattaunawa.

Ma’aikatar harkokin wajen China, ta bakin Hua Chunying, China na fatar gani an cimma daidetuwa da zaman lafiya.

Rahotanni sun ce, ministan harkokin wajen China Wang Yi ya tattauna da takwaran sa na Rasha Sergei Lavrov ta waya, inda suka amince da shirin gudanar da taro domin kawo karshen tankiyar.

Shima Sakataren harkokin wajen Amurka Rex Tillerson yace a shirye suke su tattauna da Koriya ta Arewa muddin ta amince ta aje makaman ta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.