Chicago ya maka gwamnatin Donald Trump a gaban kotu
Birnin Chicago ya maka gwamnatin Donald Trump a gaban kotu domin kalubalantar matsayin shugaban, na rikewa biranen da suka ki aiwatar da umurnin sa na kama baki marasa takardun zama kudaddensu.
Wallafawa ranar:
Shari’ar irin ta na farko na kalubalantar matsayin shugaban na neman hadin-kai wajen kama irin wadannan baki domin mayar da su kasashen su ko kuma gwamnatin tarayyar ta ki basu kudaden kula da ‘Yan Sanda.
Magajin Garin Chicago Rahm Emmanuel ya bayyana matakin a matsayin koma baya.
Babban lauyan gwamnatin Amurka Jeff Sessions ya ce ba za su bai wa biranen da suka karya doka kudin gwamnati ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu