Venezuela
Ana Zabukan Sabbin Wakilan Majalisar Kasar Venezuela Yau
Alummar kasar Venezuela na gudanar da zabukan wakilan Majalisar Dokokin kasa su 545 yau lahadi duk da boren gamagari da ake ta yi a fadin kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaba Nicolas Maduro ya bayyana cewa akwai nasara a zaben da ake yi wanda ake ganin zai kawo karshen rinjaye na wakilai 'yan adawa a majalisar.
‘Yan adawa sun bayyana kauracewa zaben na yau.
Kasashen Amurka, da kasashen kungiyar Turai, da kasashen latin America duk sun soki zaben na yau.
Watanni hudu ke nan ake ta bore a fadin kasar kuma mutane akalla 100 suka rasa rayukansu sakamakon tarzoma da ake samu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu