Isa ga babban shafi
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

An datse dala miliyan 600 daga kudaden ayyukan dakarun majalisar dinkin duniya

Wallafawa ranar:

Bayan share tsawon makonni ana tattaunawa tsakanin kasashen da ke taimaka-wa da kudade, domin daukar dawainiyar ayyukar wanzar da zaman lafiya na dakarun majalisar dinkin duniya, an cimma matsaya domin rage kudaden da kimanin dala milyan 600 a shekara. Kasar Amurka ce dai tayi ruwa tayi tsaki ganin cewa lallai sai an rage wadannan kudade saboda a cewar ta, bangaren samar da tsaro zaman lafiya a duniya na lakume makudan kudade. Kasashen Sudan ta Kudu, yankin Darfur, jamhuriyar Congo, da kasashe irin su Mali, da kuma Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, na daga cikin kasashen Afrika dake samun kudade domin daukar dawainiya irin wannan runduna ta wanzar da zaman lafiya a Afrika. Kan haka ne shirin na Ra'ayoyin Masu sauraron ya bakuk damar tofa albarkacin bakinku a kai.

Wasu daga cikin dakarun wanzar da zamanm lafiya na Majalisar Dinkin Duniya.
Wasu daga cikin dakarun wanzar da zamanm lafiya na Majalisar Dinkin Duniya. face2faceafrica
Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.