Najeriya ta fara fitar da doya zuwa kasashen Turai
Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ce, daga gobe Alhamis, za ta fara fitar da doyar da ake nomawa a kasar zuwa kasashen Turai a hukumance, in da ake matukar bukatar doyar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Ministan ayyukan noma na kasar Audu Ogbe, ya bayyana haka ga manema labarai bayan kammala taron Majalisar Ministocin kasar karkashin jagorancin mukaddashin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo a birnin Abuja.
Mr. Ogbe ya ce, a tashin farko, za a fara fitar da tan 72 na doyra zuwa Birtaniya.
Ministan ya ce, gabanin fara fitar da doyar a hukumance, Najeriya ta fitar da wani adadi na tan din doyar zuwa birnin New York na Amurka a ranar 16 ga wannan wata na Yuni.
A cewar Minista Ogbe, kididdigar hukumar bunkasa aikin noma ta Majalisar Dinkin Duniya FAO, ta nuna cewa, Najeriya na samar da kashi 61 cikin 100 na doya a duk fadin duniya.
Kasuwannin kasashen duniya na bukatar doyar da ake nomawa a Najeriya kamar yadda Ogbe ya bayyana, in da ya ce, abin kunya ne ga kasar ta gaza samar da doyar a kasuwannin.
Gwamnatin Najeriya ta ce, akwai bukatar fitar da doyar saboda akasarin wadanda ake nomawa na lalacewa ne saboda yalwarsu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu