Isa ga babban shafi
Qatar

Kasar Qatar ta Nemi Sulhu da Kasashen Larabawa

Kasar Qatar ta roki kasashen Larabawa makwabtan ta da suka janye hulda da ita da su cire mata dukkan wani takunkumi don komawa kujeran tattaunawa da ita. 

Ministan waje na kasar Qatar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman al-Thani
Ministan waje na kasar Qatar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman al-Thani Reuters
Talla

Wannan roko na zuwa ne bayan da kasar Daular Larabawa ke cewa maida Qatar saniyar ware na iya kai shekaru da yawa a haka.

Ministan Waje na kasar Qatar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al-Thani ya bayyana cewa jerin takunkumin da aka malkaya masu ya saba hankali.

Ya ce duniya ta sani cewa suna  bukatar zama a yi sulhu amma ba da rana tsaka a malkaya masu takunkumi ba.

A ranar biyar ga wannan wata ne dai Kasar Saudiya da kawayenta, Bahrain, Daular Larabawa da sauransu suka malkayawa Qatar takunkumin karairaya ta saboda zargin tana marawa kungiyoyin ta’addanci baya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.