EU za ta bai wa Sahel Euro miliyan 50 don yakar ta'addanci
Kungiyar Kasashen Turai ta amince ta bai wa kasashen Yankin Sahel Euro miliyan 50 domin kafa rundunar hadin gwiwa da za ta yaki masu tada kayar baya a Yankin.
Wallafawa ranar:
Shugabar Harkokin Diflomasiyar Kungiyar Federico Mogherini ta bayyana haka a birnin Bamako na Mali, in da ta ke cewa samun zaman lafiya a Yankin Sahel na da matukar muhimmanci ga Afrika da kuma Turai.
Jami’ar ta ce, nan bada dadewa ba za a bada kudin domin kafa rundunar wadda za ta kunshi sojoji dubu 5 daga kasashen Mali da Mauritania da Nijar da Chadi da kuma Burkina Faso.
Sai dai shugabannin na Yankin Sahel da suka gana a birnin Riyadh makwannin da suka shude, na son rubanya adadin rundunar daga dubu 5 zuwa dubu 10 saboda girman yankinsu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu