Isa ga babban shafi
Birtaniya

Batun ta'addanci ya mamaye yakin neman zabe a Birtaniya

Bayan harin da aka kai tsakiyar birnin London a ranar Asabar, barazanar hare-haren ta’addanci ne yanzu ta mamaye yakin neman zaben Birtaniya a yayin da ya rage kwanaki a gudanar babban zabe a kasar.

Mutane 34 sun mutu a cikin kasa da watanni uku sakamakon hare-haren ta'addanci a Birtaniya
Mutane 34 sun mutu a cikin kasa da watanni uku sakamakon hare-haren ta'addanci a Birtaniya REUTERS/Neil Hall
Talla

Barazanar hare-haren ta haifar da zazafarar muharawa kan matakan yaki da ta’addanci a kasar.

Rayukan mutane 34 suka salwanta a hare-haren ta’addancin da aka kai kasa da watanni uku, cikin har da wanda aka kai ranar Asabar a tsakiyar birnin London, in da mutane 7 suka mutu.

Harin dai ya sa an dakatar da yakin neman zabe na kwana guda, kuma yanzu batun barazanar hare-hare ne ya mamaye yakin neman zaben da za a gudanar 8 ga wata.

Jagoran 'yan adawa Jeremy Cobyn ya bukaci Firamista Theresa May ta yi murabus saboda yadda ‘yan sanda dubu 20 suka rasa aiki a lokacin da take rike da mukamin Ministar cikin gida a zamanin gwamnatin David Cemeron.

Jam’iyyar Labour na ganin yawan ‘yan sanda zai taimaka wajen dakile barazanar da kasar ke fuskanta a yau.

Firaminista May ta kaddamar da wani shirin yaki da ta’addanci, in da ta ce daga yanzu babu hukuncin dauri ga laifukan ta’addanci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.