Babban magatakarda na MDD Antonio Guterres, ya bukaci kasashen duniya da su gaggauta daukar matakan haramta yin amfani da makamai masu guba a duniya, a daidai lokacin da Faransa ke cewa tana da cikakkun hujjoji da ke tabbatar da cewa gwamnatin Bashar Assad ce ta yi amfani da irin wannan makami ya yi sanadiyyar mutuwar fararen hula 87 a Syria.
Guterres wanda ke gabatar da jawabi a taron da Hukumar Hana Bazuwar Makamai masu guba a duniya ta gudanar a birnin Vienna, ya ce wadannan makamai ne a matsayin barazana ga rayukan jama’a.
A game da wannan batu, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da manjo Yahya Shinku, masani lamurran tsaro, ga kuma yadda zantawarsu ta kaya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu