Isa ga babban shafi
Malaysia

Malaysia ta kori jekadan Koriya ta Arewa

Malaysia ta kori jekadan Koriya ta Arewa kan kisan Kim Jong Nam dan uwa ga shugaban kasar ta koriya ta Arewa Kim Jong-un Ma’aikatar harakokin wajen Malysia ta ba jekadan kasar sa’o’i 24 ya fice daga kasar.

Koriya ta Kudu ta zargi Koriya ta arewa da kisan Kim-Jong-nam
Koriya ta Kudu ta zargi Koriya ta arewa da kisan Kim-Jong-nam TOSHIFUMI KITAMURA / AFP
Talla

Kim Jong-Nam wanda suke uba guda da shugaban Koriya ta arewa an kashe shi ne a makwanni uku da suka gabata bayan wasu mata biyu sun barbada masa sinadari mai guba a fuska a tashar jirgin sama a Kuala Lumpur.

Kisan dai ya dada lalata dangantakar diflomasiya tsakanin Malaysia da Koriya ta Arewa inda hukumomin Kuala Lumfur suka ki mika gawar Jong-Nam ga gwamnatin Pyongyang.

Koriya ta Kudu ta fito ta zargi gwamnatin Koriya ta arewa da hannu ga aikata kisan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.