Isa ga babban shafi
Jordan

An aiwatar da hukuncin kisan mutane 15 a kasar Jordan

Hukumomi a kasar Jordan yau Asabar  suka aiwatar da hukuncin kashe wasu mutane 15 da ake zargi sun aikata lafuka barkatai tsakanin shekara ta 2006 da shekara ta 2014. 

Sarki Abdallah na biyu na kasar Jordan yana jawabi ga MDD
Sarki Abdallah na biyu na kasar Jordan yana jawabi ga MDD REUTERS/Ray Stubblebine
Talla

Ministan labarai na kasar ta Jordan Mahmud al-Momani ya tabbatar da cewa tuni mutanen na lahira kuma dukkanin su ‘yan kasar ta Jordan ne.

A cewar sa 10 daga ciki an zarge su ne da laifin ayyukan ta'addanci, yayinda biyar an zarge su ne da laifukan da suka hada da fyade.

A gidan yarin birnin Amman ne , inji Ministan aka rataye su duka.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.