Jordan
An aiwatar da hukuncin kisan mutane 15 a kasar Jordan
Hukumomi a kasar Jordan yau Asabar suka aiwatar da hukuncin kashe wasu mutane 15 da ake zargi sun aikata lafuka barkatai tsakanin shekara ta 2006 da shekara ta 2014.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Ministan labarai na kasar ta Jordan Mahmud al-Momani ya tabbatar da cewa tuni mutanen na lahira kuma dukkanin su ‘yan kasar ta Jordan ne.
A cewar sa 10 daga ciki an zarge su ne da laifin ayyukan ta'addanci, yayinda biyar an zarge su ne da laifukan da suka hada da fyade.
A gidan yarin birnin Amman ne , inji Ministan aka rataye su duka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu