Isa ga babban shafi
Greece

Za'a fara aikin ginin Masallaci na farko da izinin Gwamnatin Girka a Athens

Bayan kwashe shekaru 17 ana jinkirta ginin Masallaci a birnin Athen na kasar Girka, a yanzu haka dai ta tabbata cewa za’a fara aikin ginin masallacin na farko da izinin Gwamnati a irnin  Athens.

Firaiministan Girka Alexis Tsipras yana amsa tambayoyin manema labara game da batun bakin haure.
Firaiministan Girka Alexis Tsipras yana amsa tambayoyin manema labara game da batun bakin haure. REUTERS/Alkis Konstantinidis
Talla

Sai dai kuma wasu musulmi na cewa sai sun ga an kammala ginin ne za su yi hamdala.

Wannan gari na Athens na da musulmi akalla dubu 300.

Ana ganin kara yawan musulmi ‘yan gudun hijira daga kasashen Afghanistan, Pakistan da Masar, ya sa ake ganin mahukuntan kasar ke bada amincewarsu domin a samarda masallaci na farko da Hukumomi suka amince da shi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.