Kasashe ba su damu da kisan ‘Yan jarida ba- UNESCO
Wani rahoto da hukumar UNESCO ta fitar ya ce a cikin shekaru 10 da suka gabata, akalla ‘yan jaridu 827 ne sura rasa rayukansu a sassa daban daban na duniya. Rahoton ya yi kira ga kasashen duniya su dauki matakan kawo karshen kisan ‘Yan Jarida.
Wallafawa ranar:
UNESCO ta wallafa rahoton ne bayan tattara alkaluma akan ‘yancin aikin jarida a duniya, musamman a game da yawan ‘yan jaridar da suka rasa rayukansu tsakanin 2014-2015.
A kasashen Larabawa kawai an samu asarar rayukan ‘Yan Jarida 41 a 2014 yayin da aka kashe 37 a 2015, kamar yadda rahoton ya ce an kashe wasu ‘yan jaridun 26 a 2014 a Latin Amurka tare da kashe wasu 25 a baya.
Rahoton ya ce a nahiyar Afirka an kashe ‘yan jarida 11 a 2014 yayin da aka kashe 16 a shekarar bara. To sai dai yayin da ma’aikatan yada labarai 12 suka rasu a 2014 a yankin Asiya, shekarar da ta biyo baya ta yi muni tare da kashe akalla 22.
A dunkule dai rahoton na nuni da cewa ‘yan jarida 98 ne suka mutu akan aikinsu a 2014, inda aka kashe 115 a shekarar bara a sassa daban daban na duniya.
An wallafa rahoton ne kafin yau da aka ware a matsayin ranar yaki da cin zarafin ‘Yan Jarida a duniya
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu