Majalisar Venezuela ta gayyaci Maduro gaban ta
Majalisar Kasar Venezuela ta kada kuri’ar amincewa da bukatar gayyato shugaban kasar Nicolas Maduro dan gurfana a gaban ta dan amsa tambayoyi, bayan kotun kolin kasar ta ki amincewa da bukatar gudanar da zaben raba gardama.
Wallafawa ranar:
Ana saran shugaba Maduro ya gurfana a gaban Majalisar ranar 1 ga watan gobe kan abinda 'yan majalisun suka kira karya dokar aiki.
Kotun kolin kasar ta bayyana yunkurin tsige shugaban a matsayin wanda ya saba ka’ida.
Tuni wani sashe na 'yan adawar kasar ya amince ya zauna teburin sasantawa da gwamnati sakamakon shiga tsakani da Paparoma Francis ya yi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu