Isa ga babban shafi
Colombia

Colombia za ta kawo karshen yakin shekaru 50 a yau

Yau ne ake saran shugaban kasar Colombia Juan Manuel Santos zai sanya hannu kan yarjejeniyar kawo karshen yakin basasar kasar da shugaban kungiyar 'yan tawayen FARC, Timoleon ‘Timochenko’ Jimenez.

Shugaban kasar colombiano Juan Manuel Santos
Shugaban kasar colombiano Juan Manuel Santos REUTERS/John Vizcaino
Talla

Gwamnatin kasar ta ce, banagarorin biyu za su rattaba hannun ne da misalin karfe 5 na yamma agogon kasar a wani kasaitaccen bikin kawo karshen yakin shekaru 50.

Bikin wanda zai gudana a birnin Catargena mai dimbin tarihi, zai samu halartar sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki Moon da sakataren harkokin wajen Amurka, John Kerry da kuma wasu shugabanin kasashen Latin Amurka, da suka hada da Raul Castro na Cuba wanda kasarsa ta jagoranci tattaunawar da aka kwashe shekaru 2 ana yi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.